RMAFC Ta Nemi 'Yancin Kananan Hukumomi a Najeriya

top-news


Zaharaddeen Ishaq Abubakar, Katsina Times 

Ta Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Ba Kananan Hukumomi 'Yanci Daga Mulkin-mallakar Jihohi

Hukumar ta  "Raveneu Mobilization Allocation and Fiscal Commission" RMAFC ta nemi cikakken 'yanci ga kananan hukumomi a Najeriya, tana goyon bayan matakan da Gwamnatin Tarayya ke dauka don 'yantar da su daga ikon gwamnatocin jihohi ta hanyar tabbatar da tanade-tanaden kundin tsarin mulki.

Shugaban RMAFC, Alhaji Mohammed Bello Shehu, ya bayyana cewa kananan hukumomi na matsayin mataki na uku na gwamnati da aka kafa don samar da ingantaccen mulki a matakin tushe. Ya ce tsarin mulkin Najeriya ya amince da gwamnatocin tarayya, jihohi, da kananan hukumomi kuma kowannensu na samun kudade daga asusun tarayya.

Shehu ya yi Allah wadai da rinjayar gwamnatocin jihohi akan kananan hukumomi wanda ke hana su samun 'yancin siyasa, gudanarwa, da kudi. Wannan na hana su samar da ingantattun ayyuka a matakin tushe kamar yadda tsarin mulki ya tanada.

Ya kara da cewa rashin 'yancin siyasa na kananan hukumomi yana sa ya zama kusan ba zai yiwu ba ga al'umma su zabi shugabanninsu a wannan mataki na gwamnati wanda yake kusa da su.

A cikin jawabin, hukumar ta bayyana cewa bayar da cikakken 'yanci ga kananan hukumomi zai rage talauci da kwararar jama'a daga karkara zuwa birane, ya kawo wa mutane amfanin dimokradiyya, kuma ya jawo masu cancanta shiga takarar zabukan kananan hukumomi don inganta tsarin mulki a kowane mataki na dogon lokaci.

“Cikakken 'yanci zai kawo kyakkyawan mulki, gaskiya, da rikon amana a matakin kananan hukumomi. Matsalolin tsaro kamar ta’addanci, sace-sace, da tashin hankali na zabe za su ragu idan an tura kudaden da ake nufi da kananan hukumomi zuwa ci gaban karkara,” in ji shi. 

Shehu ya jaddada muhimmancin bayar da cikakken 'yanci ga kananan hukumomi, yana ba su damar daukar ma'aikata, sarrafa ma'aikata, tara kudade, yin dokoki, da aiwatar da ayyukansu ba tare da tsoma bakin gwamnatocin jihohi ba.

Ya ce, “'Yancin kudi na kananan hukumomi na nufin 'yancin tara haraji, samar da kudaden shiga daga hanyoyin da aka kayyade, da rarraba albarkatun kudi da kayan aiki, da yanke kasafin kudinsu ba tare da tsoma bakin wasu ba. Hakanan yana da alaka da ikon haraji, rike kudaden shiga, da hanyoyin raba kudaden tarayya bisa nauyin da aka ba kowanne mataki na gwamnati bisa tsarin mulki.” 

Shehu ya kara da cewa, "ya kamata a sani cewa tsarin mulki ya bayyana karara cewa dole ne a samar da tsarin mulkin kananan hukumomi ta hanyar zabe da dimokradiyya kuma ba a samar da wani tsarin mulki ba a matakin kananan hukumomi banda wanda aka zaba ta dimokradiyya."

Hukumar RMAFC ta nuna cewa kananan hukumomi su sami 'yancin kudi ta hanyar biyan kudaden daga asusun tarayya kai tsaye zuwa asusunsu.

Hukumar ta kuma ba da cikakken goyon baya ga karar da Gwamnatin Tarayya ta shigar tana neman izini na ba da kudaden da ke cikin asusun kananan hukumomi kai tsaye daga asusun tarayya.

Shehu ya bayyana cewa RMAFC za ta ci gaba da zama abokiyar tafiya wajen kokarin farfado da kananan hukumomi don su aiwatar da nauyin da kundin tsarin mulki ya dora musu a Najeriya, yana kira ga kungiyoyin farar hula da kafafen yada labarai su zama a sahun gaba wajen tabbatar da cewa kananan hukumomi sun samu 'yanci a Najeriya.

NNPC Advert